in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan kasashen duniya sun sake jaddada burinsu na MDGs
2013-09-26 15:46:30 cri
A rana ta biyu ta muhawarar da aka yi a babban taron M.D.D. karo na 68 a birnin New York hedkwatar M.D.D., shugaban babban taron na wannan karo John William Ashe ya gana da wasu shugabanni da kusoshin gwamnatocin kasashe da wakilansu, tare da gudanar da taron musamman bisa taken " Kara kokari don cimma burin samun bunkasuwa da aka tsara a shekarar 2000 wato MDGs. Sakatare janar na M.D.D. Ban ki-moon da shugabar hukumar shirin raya kasashe na M.D.D. Helen Clark da shugaban bankin duniya Jim Yong Kim sun halarci taron.

A cikin jawabin da Ban ki-moon ya yi, yayin da ya halarci taron, ya ce, bayan da aka tsara shirin MDGs, an samu goyon baya daga kasashen duniya, kuma sun yi alkawuran da ba a taba ganin irinsu ba, wadanda suka taimaka ga samun babban ci gaba, amma duk da haka, yanzu, akwai bambanci da ke tsakanin kasashe da yankuna daban daban na duniya wajen cimma buri 8 da ke kunshe cikin shirin na MDGs, kana akwai mutane sama da biliyan 1 da ke rayuwa cikin kangin talauci, kuma sauran shekaru 2 da rabi cikin wa'adin da aka tsara na cimma wannan burin.

Ban ki-moon ya ce, akwai kalubale sosai don cimma burin, amma mun yi imani cewa, za a kammala wadannan ayyuka cikin wannan lokaci da aka tsaida. Haka kuma, gwamnatocin kasashen duniya, da bankin duniya da hukumomi masu zaman kansu da sauran hukumomi sun dauki sabon alkawari, wato suna fata za su kara saka jarin da yawansa ya kai dalar Amurka biliyan 2.5 don cimma burin. Dole ne kasashen duniya su cimma burin MDGS, don kawo wani harsashi mai kyau wajen tsara shirin samun dauwamammen ci gaba bayan shekarar 2015.

Shugabanni da kusoshin gwamnatoci da wakilan kasashen duniya sun cimma matsaya guda tsakaninsu a yayin taron, inda suka jaddada kokarin cimma burin na MDGs, tare da dora muhimmanci sosai game da matsalar bambanci da rashin daidaito wajen samun ci gaba da ke kasancewa a yanzu. Haka kuma, mahalartar taron sun amince da kiran taron koli a watan Satumba na shekarar 2015, don tsara shirin samun ci gaba bayan shekarar 2015.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China