in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
M.D.D. ta yi kira ga kasashen duniya da su ba da kudin tallafi wajen yaki da cutar zazzabin cizon sauro
2013-04-26 16:40:31 cri
Ranar 25 ga watan Afrilu rana ce ta yaki da cutar zazzabin cizon sauro ta kasa da kasa, taken ranar wannan shekara shi ne zuba jari don samun makoma mai kyau wajen cimma nasarar yaki da cutar.

A wannan rana, sakatare janar na M.D.D. Ban ki-moon ya yi jawabi, inda ya yi kira ga kasashen duniya da su ba da kudin tallafi wajen yaki da cutar, da sa kulawa sosai ga wadanda suke fama da cutar, da taimakawa wajen gano sabbin hanyoyin yaki da cutar. Ban da wannan kuma, Ban ki-moon ya yi nuni cewa, yanzu, kasashen duniya na nuna jinkiri ga kara ba da tallafin kudi sosai wajen yaki da cutar, dalilin haka ne, ake samun tafiyar hawainiya wajen daukar matakan yaki da cutar, da rarraba gidajen sauro. Haka kuma, ya bukaci hukumomin kiwon lafiya na kasashen duniya, cikinsu har da gwamnatocin kasashen da ke fama da cutar zazzabin cizon sauro da su cika alkawarin da suka dauka wajen kara samun hanyoyin rigakafin cutar, ta yadda, za a kawo karshen wahalar da masu fama da cutar suke sha.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China