in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kafa shirin ko-ta-kwana wajen yaki da mahaukaciyar guguwar iska
2013-09-23 17:01:25 cri
A ranar 23 ga wata, domin magance hasarar da mahaukaciyar guguwar iska ta Tiantu ta kawo wa lardin Guangdong na kasar Sin a bana, hukumar rage bala'i ta kasar Sin da ma'aikatar kula da harkokin cikin gida ta kasar, sun kafa shirin ko-ta-kwana don yaki da bala'i da ceton mutane, kuma sun tura rukunin aiki zuwa yankunan da bala'in ya shafa, don gudanar da aikin ceton mutane.

Bisa rahoton da hukumar kula da harkokin cikin gida ta lardin Guangdong ta bayar, ya zuwa ranar 23 da karfe 8 na safe, mutane kimanin miliyan 3 da dubu 563 suka gamu da mahaukaciyar guguwar iska ta Tiantu, cikinsu mutane 25 sun rasu, kana kuma an kauratar da mutanen da yawansu ya kai dubu 226, sannan bala'in ya haddasa lalacewar gidaje 7100 da hasarar dukiyoyin na kimanin kudin Sin Yuan biliyan 3.24.

Ya zuwa yanzu, hukumar rage bala'i da hukumar kula da harkokin cikin gida ta lardin Guangdong sun kafa shirin ko ta kwana cikin gaggawa, don tura rukunin aiki zuwa yankunan da bala'in ya shafa, wajen taimaka wa jama'a da suka gamu da bala'in farfado da zaman rayuwarsu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China