Ya ce, hakika ba mu ji dadi ba, domin sifetocin MDD ba su mayar da hankali sosai kan shaidun Syria ba, ganin cewa, a fili suke kuma suna da muhimmanci, don haka, kwararrun kasar Rasha za su yi nazari a kansu.
A ranar Talata ne wata tawagar kasar Rasha ta isa kasar Syria, domin ta tattauna da jami'an kasar game da yarjejeniyar baya-bayan da aka cimma tsakanin Rasha da Amurka da nufin daidaita batun zargin da ake yiwa kasar na kai hari da makamai masu guba.
Kasar Rasha ta gabatar da wani shiri na sanya makaman Syria masu guba karkashin sa-idon kasa da kasa, don hana yiwuwar Amurka na kai mata harin soja, bisa zargin da ake yiwa sojojin Syria na amfani da makamai masu guba kan fararen hula a wajen Damascus a ranar 21 ga watan Agusta.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mista Hong Lei, ya bayyana a ranar 18 cewa, kasar Sin tana mara wa kwamitin sulhu na MDD baya don ya taka muhimmiyar rawa kan batun da ya shafi zaman lafiya da tsaro. Haka kuma, a cewar Mista Hong, kasar Sin na fatan ganin an warware maganar makamai masu guba na kasar Sham ta hanyar siyasa, da gudanar da aikin lalata makaman karkashin tsarin MDD, yayin da ake kokarin daidaita batun ta hanyar shawarwari. Kasar Sin a nata bangaren na son mu'ammala da bangarorin da batun da ya shafa, in ji Mista Hong. (Ibrahim)