in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Syria ya amince da mika makamai masu guba
2013-09-13 09:57:19 cri
Shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya ce, ya amince ya sanya makamai masu guba karkashin kulawar kasa da kasa, kamar yadda kasar Rasha ta bukata, amma ba domin barazanar da kasar Amurka ta yi ba.

Shugaban a cikin wata hira da ya yi da kafar watsa labarai ta Rasha '24 channel', kuma kamfanin dilancin labarai na kasar Syrian ta ruwaito, ya ce, ko duk wani irin yaki da aka kai kan kasar Syria zai shafi yankin gaba daya kuma zai saka daukacin yankin a cikin tarin matsaloli da rashin kwanciyar hankali na shekaru masu zuwa nan gaba.

A cewar kamfanin dillancin labaran kasar Syria SANA, wannan furuci na shugaba Assad ya zo ne kwanaki bayan da gwamnatinsa ta amince da tayin da kasar Rasha ta yi mata game da mika makamanta masu guba karkashin sa idon kasa da kasa, don kaucewa harin soja da Amurka ke barazanar kai wa kasar bisa zargin kai hari da makamai masu guba a Damascus a watan da ya gabata.

A sakamakon shiga tsakanin Rasha, shugaba Assad ya ce, aiwatar da wannan niyya ta gwamnatinsa, ya danganta ne ga bangaren Amurka idan ta amince ta jingine duk wani kiyayya da take nuna ma kasarsa. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China