in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fadada filin jiragen sama na kasa kasa a Lome yadda ya kamata
2013-01-05 16:35:43 cri
Ranar Jumma'a 4 ga wata, 'yan majalisar dokokin kasar Togo fiye da 30 sun ziyarci wurin da ake aikin fadada da kuma yin kwaskwarima ga filin jiragen sama na kasa da kasa da ke birnin Lome, hedkwatar kasar, wanda aka sanya wa sunan marigayi janar Gnassingbe Eyadema.

Yanzu ana gudanar da aikin yadda ya kamata. Kwararrun kasar Sin a fannin gine-gine da ma'aikatan kasar Togo suna hada kansu sosai ba tare da wata matsala ba. Kuma ana sa ran cewa, nan da shekaru 2 masu zuwa za a kammala aikin kuma za a fara amfani da filin jiragen saman.

An labarta cewa, sabon bangaren tashi da saukar fasinja mai benaye 2 zai raba fasinjojin da suka sauka da wadanda suke shirin tashi. Sa'an nan kuma filin jiragen saman zai kara yawan fasinjojin da zai yi jigilarsu a ko wace shekara daga dubu 400 zuwa miliyan 2, kana kuma, zai kara yawan kayayyakin da zai yi jigilarsu a ko wace shekara daga ton dubu 10 zuwa ton dubu 50.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China