in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Sin da Togo sun yi murnar cika shekaru 40 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu
2012-09-19 14:19:50 cri
A ranar 19 ga wata, shugaban kasar Sin Hu Jintao da takwaransa na kasar Togo Faure Essozimna Gnassingbe sun buga waya ga juna don taya murnar cika shekaru 40 da kula dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Hu Jintao ya bayyana cewa, a shekaru 40 da suka gabata, tsofaffin shugabannin kasashen biyu sun kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu, wanda ya bude kafar sada zumunta a tsakanin kasashen biyu. A cikin shekaru 40 din, kasashen biyu sun sada zumunci, yin mu'amala bisa matsayin zaman daidai wa daida, yin hadin gwiwa da samun moriyar juna, kana sun inganta dangantakarsu yadda ya kamata, wadda ta zama abin koyi ta fuskar hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa. Kasar Sin tana son yin amfani da damar cika shekaru 40 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da Togo, don yin mu'amalar sada zumunta da fadada yin hadin gwiwa a tsakaninsu, a kokarin inganta dangantakarsu zuwa wani sabon matsayi, kuma wannan zai taimakawa al'ummominsu.

Shugaba Faure ya ce, kasahen Togo da Sin sun fahimci juna ta fannin siyasa, da kuma samun moriyar juna a fannin tattalin arziki. A cikin shekaru 40 da suka wuce, bangarorin biyu sun yi hadin gwiwa a fannonin aikin gona, ayyukan more rayuwa, kiwon lafiya, bada ilmi da dai sauransu, wanda ya kawo babbar moriya gare su. Kasar Togo tana son yin kokari tare da kasar Sin wajen ci gaba da sa kaimi ga samun wadata da juna. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China