in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na mai da hankali sosai kan yiwuwar daukar matakan soja kan Syria da wasu kasashe za su yi
2013-09-02 19:49:46 cri
A yau Litinin 2 ga wata a nan birnin Beijing, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei yayi bayani game da tsanantar yanayin da ake ciki a kasar Syria a fannin amfani da makamai masu guba cewa, Sin bata amince da kowa yayi amfani da makamai masu guba ba, kuma ta nuna goyon baya ga MDD da ta yi bincike iri na zaman kanta cikin adalci.

Har wa yau game da bayanin shugaban kasar Amurka Barack Obama na cewa, kasar ta yanke shawarar daukar matakan soja kan kasar Syria, Hong ya furta cewa, kasar Sin ta dade tana mai da hankali kan yanayin Syria, kuma tun asali tana ganin cewa, ba za a iya daidaita batun Syria ba sai dai ta hanyar siyasa. Sin ta mai da hankali sosai kan yiwuwar daukar matakan soja kan kasar Syria da wasu kasashe za su yi. Kamata ya yi kasa da kasa su bi kundin tsarin mulkin MDD da ka'idojin dangantakar kasashen duniya yayin da suke daukar matakai, a kokarin kauracewa tsanantar yanayin da ake ciki a Syria, da kara kawo illa ga yankin Gabas ta Tsakiya.(fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China