in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan kudin da za a samu a fannin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Afrika da kasar Sin zai kai wani sabon matsayi a tarihi
2010-12-03 21:36:23 cri

Ranar 2 ga wata a ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Uganda, ya ba da rahoton dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Afrika da kasar Sin. Rahoton ya bayyana cewa, yawan kudin da kasar Sin da Afrika suka samu ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu a bana zai kai ko kuma zai zarce dala biliyan 106.8 wato matsayin koli da aka samu a shekarar 2008.

Wannan rahoto ya kasance rahoton farko da hukumar cinikayya ta kasar Sin ta bayar dangane da dangantakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakanin kasar Sin da Afrika, wanda ya waiwayin ci gaban dangantakar bangarorin biyu a cikin shekaru 60 da suka gabata, kuma ya yi tsinkaye kan ci gaban da za su samu wajen hadin kai ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu.

A gun bikin gabatar da rahoton, jakadan kasar Sin dake kasar Uganda Sun Heping ya ce, dangantakar hadin kai bisa manyan tsare-tsare a fuskar tattalin arziki da cinikayya dake tsakanin kasar Sin da Afrika ba ma kawai za ta yi amfani ga bangarorin biyu ba, har ma za ta kawo tasiri ga zaman lafiya, karko da bunkasuwar duniya.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China