in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta zama abokiyar cinikayya mafi girma ga kasashen Afirka
2011-11-17 21:05:36 cri
A ran 16 ga wata, ma'aikatar harkokin kasuwanci ta kasar Sin ta ba da labari cewa, daga shekarar 2001 zuwa shekarar 2011 matsakaicin yawan cinikayya da aka yi tsakanin kasashen Sin da Afirka ya karu da kashi 28 cikin dari a kowace shekara, haka kuma kasar Sin ta zama abokiyar cinikayya mafi girma ga kasashen Afirka.

Wani mai kula da harkokin ciniki na ma'aikatar harkokin kasuwanci na kasar Sin ya bayyana cewa, a cikin 'yan shekarun nan, dangantakar cinikayya dake tsakanin kasashen Sin da Afirka ya bunkasa a cikin sauri a fannoni daban daban, kuma ta zama abokiyar hadin gwiwa a duk fannoni wadda ke da muhimmanci ga bunkasuwar al'ummomin da tattalin arziki na bangarorin biyu. Kasar Sin ita ce sahihiyar aminiya ta Afirka, za ta yi musayar ra'ayoyi kan harkokin bunkasuwa tare da kasashen bisa ka'idojin na zaman daidaici da moriyar juna da neman bunkasa tare. Bugu da kari, kasar Sin ta nuna goyon baya da taimako ga kasashen Afirka ta hanyar zuba jari da ba da gudumawa, don tabbatar da moriyar juna da samun bunkasawa tare a tsakaninsu. (Zainab Zhu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China