in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron manyan jami'an kula da albarkatun ruwa na duniya ya yi kira da a kara yin hadin kai da shawarwari
2013-08-23 16:03:00 cri
An kammala taron manyan jami'ai kan batun albarkatun ruwa na tsawon kwanaki uku a ran 22 ga wata a birnin Dushanbe hedkwatar kasar Tajikistan, inda aka zartas da wata sanarwar yin kira ga kasa da kasa da su kara hadin gwiwa da yin shawarwari kan batun albarkatun ruwa.

Sanarwar ta ce, a ganin mahalartan taro, gwamnatocin kasashe daban-daban suna ba da babban taimako wajen sarrafa albarkatun ruwa, hakan ya sa, an yi kira ga kasashen dake mallakar mafarin ruwa gaba daya da su kara hadin kai da tuntubar juna bisa dokar kasa da kasa ta yadda za su ingiza bunkasuwar kasa da kasa.

Haka zalika sanarwar ta yi kira ga kasashen dake mallakar mafarin ruwa gaba daya su sarrafa wadannan matattarun ruwa ta yadda za su kasance wani tushe ga ayyuka da dama da wadannan kasashe za su amfana a nan gaba, ciki hadda samun bunkasuwa mai dorewa, kawar da talauci da yunwa, tabbatar da isashen hatsi, tinkarar sauyin yanayi, kiyaye muhalli, yin rigakafin bala'u daga indallahi, da kuma tabbatar da bunkasuwar birane da kauyuka cikin dogon lokaci har ma da kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa. Mahalartan taron sun yi alkawarin cewa, za su mai da albarkatun ruwa a matsayin wani mataki ne da aka dauka domin kiyaye amincewar juna da hadin gwiwa tsakanin kasashe daban-daban da kuma raya kasashensu gaba daya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China