in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Angola ta zamo zakara a gasar FIBA ta 'yan wasa 'yan kasa da shekaru 16
2013-07-13 20:44:50 cri
Kasar Angola ta lashe gasar kwallon kwandon nahiyar Afirka ta 'yan wasa ajin 'yan kasa da shekaru 16 da haihuwa, wanda aka kammala ranar Lahadin data gabata a kasar Madagaska. Yayin wasan karshe da aka buga tsakanin kungiyar 'yan wasan Angola da na Masar, Angolan ce ta lashe gasar da maki 75, yayinda kasar Masar ta samu maki 66.

An dai kai ruwa rana a zango na 4 na wasan, kafin Angolan ta samu wannan nasara. Da wannan nasara da Angolan ta samu ta zamo a matsayi na farko, cikin jerin kasashen da suka shiga gasar, sai kuma Masar dake biye mata, inda kuma kasar Tunusiya ta zamo ta uku, sai kuma Madagaska dake matsayi na Hudu.

An dai fara wannan gasa ajin matasa 'yan kasa da shekaru 16 ne a ranar 28 ga watan Yunin da ya gabata, inda kasashe 10 da suka hada da Madagaska, da Tunusiya, da Cote d'Ivoire da Algeriya suka fara fafatawa. Ragowar kasashen da suka shiga gasar sun hada da Gabon, da Masar, da Angola, da Mozambique, Kamaru da kuma dimokaradiyyar Congo.

Wannan dai dama da Angola ta samu ya ba ta zarafin shiga gasar kwallon Kwando ta duniya, wadda zata gudana a birnin Dubai a shekarar badi. Wannan ne kuma karo na Uku da kasar Madagaska ta dauki bakuncin manyan gasanni, bayanda ta dauki bakuncin makamanciyar wannan gasa ta mata a shekarar 2009, da kuma ta ajin maza a shekarar 2012.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China