in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya yi kiran daukar matakin siyasa don warware rikicin kasar Syria
2013-03-16 16:42:12 cri
Shugaban hukumar 'yan gudun hijira ta MDD (UNHCR) Antonio Guterres a ranar Jumma'ar nan ya yi kiran a nemo hanyar siyasa don warware rikicin kasar Syria cikin hanzari.

Bayan rangadin da ya kai a ofishin rajista ta hukumar 'yan gudun hijiran dake garin Tripoli a yankin arewacin tekun kasar Lebanon, Guterres ya ce rikicin na Syria na kawo tabarbarewar lamura a yankin da ma duniya baki daya don haka ya yi kira ga kasa da kasa su ba da karin taimako ga kasashen dake lura da 'yan gudun hijira.

Jami'in na MDD ya nanata godiya ga kasar Lebanon da jama'arta dangane da dimbin tallafi da suke baiwa 'yan gudun hijiran.

Hukumar 'yan gudun hijira ta MDD a cikin rahotonta na baya bayan nan ta ce yawan mutanen kasar Syria dake gudun hijira a kasar Lebanon ya kai dubu 336. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China