in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta ci gaba da yin kira ga kasa da kasa da su cika alkawarinsu na ba da agaji ga kasashen Afirka
2013-06-14 19:47:14 cri
A ranar Jumma'a 14 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan Habasha, Hailemariam Dessalegn a nan birnin Beijing, inda ya ce, Sin za ta ci gaba da yin kira ga bangarori daban daban da su girmama bukatun nahiyar Afirka na bunkasa cikin 'yanci, da cika alkawarinsu na ba da agaji ga kasashen Afirka, a kokarin taimaka musu wajen samun karin ci gaba.

Xi ya ce, kamata ya yi kasashen Sin da Habasha su karfafa mu'amala tsakanin manyan jami'ansu, da zurfafa hadin gwiwa tsakaninsu a muhimman fannoni. Sin ta nuna goyon baya ga Habasha wajen shiga kungiyar cinikayya ta duniya WTO.

Ban da haka, Xi ya taya wa kungiyar AU murnar cika shekaru 50 da kafawa, ya ce, Sin za ta nuna goyon baya ga kasashen Afirka wajen samun ci gaba tare.

A nasa bangare, firaministan kasar Habasha Hailemariam ya ce, Sin ta kafa manufarta kan Afirka bisa adalci, girmamawa juna, da kuma moriyar juna. Dukkan kasashen nahiyar suna maraba sosai da wannan tsari. Da fatan za a karfafa dangantakar abokantaka a duk fannoni tsakaninsu bisa dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, a kokarin samun ci gaba tare. Habasha za ta ci gaba da ba da gudummawa wajen sa kaimi ga raya dangantaka tsakanin bangarorin biyu.

A wannan rana kuma, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, Zhang Dejiang shi ma ya gana da mista Hailemariam a birnin Beijing.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China