in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin gwamnatin Sin ya yi shawarwari da ministar harkokin wajen kasar Ghana
2013-03-22 16:38:19 cri
A ranar 21 ga wata, manzon musamman na gwamnatin Sin game da batun kasashen Afrika Zhong Jianhua ya gana da ministar harkokin waje da hadin gwiwar kasashen Afrika ta kasar Ghana Madam Hannah Teteh, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra'ayi game da raya dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da halin tsaro da ake ciki a kasashen Afrika.

Mr. Zhong ya ce, a cikin 'yan shekarun nan, dangantakar tsakanin kasashen Sin da Ghana ta bunkasa cikin armashi, kuma hadin gwiwa daga dukkan fannoni a tsakaninsu ya habaka cikin hanzari, kuma jama'ar kasashen biyu sun samu alfanu daga cikinsu, tare da fatan ganin an kara zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Teteh ta bayyana cewa, bayan da aka kafa dangantakar diplomasiyya tsakanin kasashen Ghana da Sin a cikin shekaru sama da 50 da suka gabata, Sin ta samar da taimako maras jin kai gami da nuna goyon baya ga kasar Ghana, musamman ma a cikin shekarun nan da ake ciki, Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen gina muhimman kayayyakin more rayuwa a Ghana, abin da ya ba da babbar gudummawa wajen raya zamantakewar al'umma da tattalin arziki na wurin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China