in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya gana da wasu shugabannin Turai kan yadda za a bunkasa alaka da tafiyar da harkokin kasa da kasa
2019-03-27 09:17:21 cri

A jiya Talata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da shugaban hukumar zartaswar EU Jean-Claude Junker, inda suka amince su karfafa alakar dake tsakanin Sin da EU, da ma yadda ake tafiyar da harkokin kasa da kasa.

Shugabannin sun gana ne a kasar Faransa a gefen taron dandalin tafiyar da harkokin duniya da kasashen Sin da Faransa suka jagoranta tare.

Shugaba Xi ya kuma lura da yadda ake kara samun tashe-tashen hankula da nuna kariya ga harkokin cinikayya da yanayi na rashin tabbas a duniya. Ya ce, a shirye kasar Sin ta ke, ta yi aiki da sauran bangarori, ta yadda za a kare manufar cudanyar kasashen duniya, da inganta yadda ake tafiyar da harkokin kasa da kasa, da ma hada kai don magance kalubalen da duniya ke fuskanta.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China