in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta fitar da shawarwari ga matafiya na kasa da kasa game da barkewar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2018-05-31 10:46:41 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta fitar da shawarwari ga matafiya tsakanin kasa da kasa, game da barkewar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, biyo bayan sabon yanayin da ake ciki game da cutar a jiya Laraba.

Hukumar ta ce hadarin kamuwa da cutar ga masu shiga kasar ba shi da yawa, domin mutane kan kamu da ita ne bayan sun fara fama da alamomin da suka hada da zazzabi da rashin kwarin jiki da ciwon damatsa da na makwogwaro.

Hukumar ta shawarci masu tafiya kasar, su tuntubi likita a kalla makonni 4 zuwa 8 kafin tafiyarsu. Inda ta ce ya kamata tuntubar ta kunshi bayanai game da muhimman haduran lafiya da za a iya gamuwa da su, da tantance bukatar rigakafi da na maganin zazzabin cizon sauro da kuma gano ko akwai wasu kayayyakin lafiya da ake bukatar matafiyi ya dauka. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China