Har wa yau bisa jadawalin na FIFA, kulaf din kasar Cote d'Ivoire ne na daya a nahiyar ta Afirka, sai kuma Masar dake biye a matsayi na 2 yayin da kuma Algeria ke a matsayi na 3.
Game da kulaflikan kasashen duniya dake kan gaba a wancan jadawali kuwa, kasar Sifaniya ce ke ci gaba da rike kambin ta a matsayi na daya, za kuma ta kara a rukuni guda tare da Ghana, a gasar cin kofin duniya dake tafe. A matsayi na biyu kuwa kulaf din kasar Jamus ne ke biyewa Sifaniya, yayin da kuma kulaf din kasar Portugal ke matsayi na 3.
Bugu da kari hukumar ta FIFA ta ce, a kalla kulaflikan kasashe 143 ne suka rike matsayin da suke kai a watan Afirilu, a sabuwar kididdigar da ta fitar a wannan wata na Mayu.