Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin ta riga ta dauki matakin da ya dace don kawar da talauci a kan lokaci
2020-08-10 19:59:31        cri
Ofishin yada labarai na gwamnatin kasar Sin, ya kira wani taron manema labarai a yau Litinin, inda ya bayyana cewa, ya zuwa karshen shekarar 2019, kaso 95% na jimillar matalautan kasar sun fito daga kangin talauci, kuma kaso 90% na gundumomi masu fama da talauci a kasar sun kai ga fita daga wannan mawuyacin hali.

Mataimakin darektan ofishin ba da jagoranci ga aikin kawar da talauci na gwamnatin kasar Sin Ou Qingping, ya shaidawa manema labarai a gun taron cewa, ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Sin ta riga ta dauki matakin da ya dace, kan wasu mutane da suke cikin kangin talauci, don taimaka musu fita daga wannan mawuyacin hali.

A cewar Ou, yanzu haka an samarwa dukkanin matalauta inshorar jiyya. A hannu guda kuma, cutar COVID-19, da kuma bala'in ambaliyar ruwa, ba za su dakatar da aikin kawar da talauci, da hana samun ci gaba a wannan fanni ba. (Amina Xu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China