Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Xi Jinping ya jajantawa takwaransa na Tanzaniya saboda rasuwar tsohon shugaban kasar Benjamin Willjam Mkapa
2020-07-31 21:06:43        cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya isar da sakon jaje ga takwaransa na kasar Tanzaniya, John Pombe Joseph Magufuli, kan rasuwar tsohon shugaban kasar Benjamin Willjam Mkapa, ya kuma jajantawa iyalan mamacin.

Shugaba Xi ya ce, marigayi Mkapa fitaccen shugaba ne a kasar Tanzaniya har ma a nahiyar Afirka, kuma aboki na kwarai ga kasar Sin, wanda ya bayar da babbar gudummawa ga yaukaka dangantakar dake tsakanin Sin da Tanzaniya da ma Afirka baki daya.

Xi ya ce yana maida hankali sosai ga raya huldar kasashen biyu, yana kuma fatan ci gaba da kokari tare da shugaba Magufuli, wajen ciyar da dangantakar abokantakarsu bisa manyan tsare-tsare gaba, da kara kawo alfanu ga daukacin jama'ar sassan biyu. (Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China