Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jaridar Wall Street Journal: tattalin arzikin kasar Sin ya samu tagomashi
2020-07-17 11:08:13        cri

Jaridar Wall Street, ta wallafa a jiya cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya dawo bisa turbar ci gaba, inda ya samu tagomashi a rubu'i na biyu na bana, lamarin da ya sa kasar ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya ta yi nesa da shiga matsalar tattalin arziki, yayin da wasu kasashe ke ta fama da tasirin COVID-19.

Da farko a jiyan, kasar Sin ta fitar da rahoton da ya bayyana karuwar tattalin arzikinta da kaso 3.2 a cikin rubu'i na 2 na bana.

Jaridar ta ce, harkokin kasuwanci na kasar Sin sun cike gibin dake akwai wajen samar da kayayyaki a duniya, tare da fadada fitar da kayayyaki, saboda kamfanonin kasar sun fara aiki kafin na sauran kasashen duniya dake fitar da kayayyaki.

Rahoton da jaridar ta wallafa mai taken "Da alamu tattalin arzikin kasar Sin ya farfado, amma har yanzu akwai kalubale" ya kuma bayyana cewa, akwai banbanci sosai ga kamfanonin kasashen waje dake aiki a ciki da wajen Sin.

Sai dai, takardar ta ce babbar barazana ga kasar Sin ka iya zama Amurka, inda manyan jami'an kasar da 'yan majalisun dokoki daga dukkan manyan jam'iyyun kasar biyu, ke kara matsawa Sin lamba da kakaba takunkumi kan jami'ai da kamfanonintan, gabanin zaben shugaban Amurka dake tafe cikin watan Nuwamba. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China