Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta bukaci Amurka da ta dakatar da tsoma baki a harkokin cikin gidan ta da sunan addinai
2020-06-11 20:36:49        cri

Madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana yau Alhamis a nan Beijing cewa, kasar Sin ta bukaci Amurka da ta girmama hakikanin abubuwa, ta daina kallon duniya bisa ra'ayinta, ta dakatar da tsoma baki a harkokin cikin gida na kasar Sin da sunan addinai.

Madam Hua ta bayyana haka ne, yayin da take mayar da martani kan rahoton da Amurka ta gabatar a kwanan baya, inda ta soki manufofin kasar Sin ta fuskar addinai. Madam Hua ta kara da cewa, akwai damuwa matuka kan yadda al'ummomi marasa rinjaye suke bin addini a Amurka. A duk lokacin da Amurka ta fitar da irin wannan rahoto, ta kan bayyana rashin gaskiyarta da ma fuska biyu da take nunawa kan harkokin addini. (Tasallah Yuan)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China