![]() |
|
2020-05-11 10:52:41 cri |
Ya ce, kasashen Amurka da Turai ba su dauki matakan da suka dace ba, bayan barkewar cutar a sauran kasashen duniya a kalla da wata daya, har sai da cutar ta fara yaduwa a kasashen Amurka ta Turai, wato dai sun sami damar shiryawa yadda ya kamata, amma suka kasa. Ya ce ci gaban karuwar mutanen da suka kamu da cutar, da karuwar adadin rasuwar mutane, da kuma matsalar kasa samun ayyukan yi da al'ummomin kasashen suke fama da ita, dukkansu sun nuna cewa, wadannan kasashe ba su warware matsalar cutar COVID-19 yadda ya kamata ba.
Bugu da kari, ya yi Allah wadai da ra'ayoyin kasashen yammacin duniya, yana mai cewa, halayensu na kaunar kudade da kayayyaki, ya sa, ba su kula da tsoffafi, da masu fama da talauci da sauran mutane marasa karfi yadda ya kamata ba, wanda kuma hakan shi ne daya daga cikin dalilan da suka sa suka fadi jarrabawar cutar COVID-19. (Maryam)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China