![]() |
|
2020-04-27 13:29:38 cri |
Ya kuma kara da cewa, dukkanin al'ummomin kasar Sin sun cimma matsayi daya da kuma yin hadin gwiwa wajen yaki da cutar numfashi ta COVID-19. Ya ce, yadda kasar Sin ta gina asibitoci masu inganci guda biyu cikin kwanaki 10, da kuma sa kaimi ga al'ummomin kasar da su ba da taimako ga birnin Wuhan ya burge shi kwarai da gaske. Kuma dukkanin jita-jitar da aka yi kan sakamakon da kasar Sin ta cimma wajen yaki da cutar numfashi ta COVID-19 ba su da tushe. A cewarsa ya dace kasashen Afirka su koyi fasahohin kasar Sin, da kyautata ayyukan gina ababen more rayuwa, da habaka ayyukan kimiyya da fasaha domin ci gaba da karfafa ayyukanta na fuskantar kalubaloli. (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China