Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin ta kara bayar da gudummowa ga Zimbabwe don yaki da COVID-19
2020-04-24 09:46:28        cri
Kasar Sin ta sake bayar da gudummowar kayayyakin lafiya ga kasar Zimbabwe, tallafin ga kasar da ke kudancin Afrika zai taimaka mata wajen ayyukan yaki da cutar COVID-19.

Jakadan kasar Sin a Zimbabwe Guo Shaochun, shi ne ya jagoranci bikin mika gudummowar kayayyakin lafiyar ga shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa a fadar shugaban kasar.

Kayayyakin sun hada da takunkumin rufe fuska 166,000, da rigunan baiwa jami'an lafiya kariya 7,600, da kayayyakin gwaje gwaje 20,000, sai safar hannu 12,000, da kuma na'urorin taimakawa numfashi guda biyar. (Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China