2020-04-20 09:54:56 cri |
Cikin rahoton da ta fitar a jiyan, cibiyar Africa CDC ta kuma bayyana cewa, kawo yanzu, an samu bullar cutar a kasashen nahiyar 52, inda kuma ta fi kamari a kasashen Masar da Afrika ta Kudu da Algeria da kuma Morocco.
Yayin wani taron manema labarai ta kafar bidiyo a ranar Jumma'a, daraktan cibiyar John Nkengasong, ya bayyana muhimmancin dake tattare da karfafa daukar matakan kandagarki a fadin nahiyar domin dakile ci gaba da yaduwar cutar.
Ya kara da cewa, matakin takaita zirga-zirga da kasashen nahiyar suka dauka ka iya illa kan harkokin tattalin arziki da zamantakewa, amma alfanun da zai yi a nan gaba na da yawa. Yana mai cewa, zai ceci rayuka tare da taimakawa wajen gaggauta kawo karshen annobar. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China