![]() |
|
2020-04-13 10:02:16 cri |
Uku daga cikin mutanen da ake zargin sun samu harbin bindiga a lokacin da aka yi musayar wuta tsakaninsu da jami'an tsaron, a cewar Bola Longe, babban jami'in 'yan sandan jihar Nasarawa.
A cewar Longe, ana tuhumar mutanen da aikata laifuffuka daban daban da suka shafi yin garkuwa da mutane a fadin jihar.
Jami'in ya ce, tuni mutanen da aka kubutar daga hannun masu garkuwar sun riga sun koma cikin iyalansu, an yi nasarar kubutar da su ne bayan samun wasu bayanan sirri game da ayyukan masu garkuwar.(Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China