![]() |
|
2020-04-13 09:51:06 cri |
A sanarwar da John Enenche, kakakin rundunar tsaron Najeriya ya fitar, ya ce dakarun sun kaddamar da samamen ne a ranar Lahadi a yankunan jihar Naija.
Eneche ya ce, 'yan bindigar sun tsere, inda suka bar mutanen da suka yi garkuwar da su bayan mummunan musayar wuta da suka yi da dakarun tsaron kasar.
A cewar kakakin rundunar tsaron, an yi garkuwa da mutanen ne tun a ranar 27 ga watan Maris, inda suke tsare da su a wani waje da ba'a tantance ba a shiyyar tsakiyar Najeriya.(Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China