2020-03-28 17:05:57 cri |
Bangaren Sin ya bayyana cewa, kasar ta dauki matakan da suka dace kuma bisa tushe, don mayar da martani kan matsin lambar da Amurka da ta dade t na yi wa kafofinta na watsa labarun dake kasar.
Bangaren Sin ya kuma jaddada cewa, ko da yaushe kasar Sin na maraba da 'yan jaridar kasashen ketare su gudanar da ayyukansu bisa doka da ka'ida a kasar. Amma abubuwan da kasar Sin ke adawa su su ne, rainata da ake yi da yada labarun karya bisa hujjar 'yancin watsa labaru, da kuma ayyukan saba wa da'ar sana'ar watsa labaru. Idan kafofin watsa labarun uku ba su ji dadin matakan ba, sai su bayyana korafinsu ga gwamnatin Amurka.(Bilkisu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China