Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka wajaba wajen kare hakkoki da muradun kamfanoninta
2019-08-09 10:51:31        cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta ce kasar za ta tsaya tsayin daka wajen mara baya ga kamfanonita domin daukar matakan da suka halatta, na kare hakkoki da muradunsu, kuma za ta ci gaba da daukar dukkan matakan da suka wajaba wajen kare wadancan hakkoki.

Rahotanni sun ce hukumar kula da ayyuka ta Amurka, ta fitar da wani umarni na wucin gadi, wanda ya haramtawa dukkan hukumomin gwamnati sayar da kayayyakin sadarwa da bada hidimomi ga kamfanoni biyar na kasar Sin, ciki har da kamfanin Huawei, bisa dogaro da tanadin dokar kasafin kudi na hukumar tsaron Amurka na shekarar kudi ta 2019.

Da take amsa tambayar da manema labarai suka yi mata dangane da batun, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin, Hua Chunying, ta bayyana rashin gamsuwar kasar Sin da kuma adawa da dabi'ar Amurka, na nuna wariya da daukar matakan da ba su dace ba a kan wasu kamfanonin Sin, bisa wasu munanan bayanai kan kasar Sin dake kunshe cikin dokar kasafin kudin hukumar tsaron Amurkar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China