Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Fashewar bututun mai a Najeriya ta raba mutane 276,000 da muhallansu
2020-03-20 11:19:59        cri
A kalla mutane 276,000 suka rasa muhallansu sakamakon mummunar fashewar bututun mai da ya faru a yankin Amuwo-Odofin mai yawan cunkuson jama'a dake jihar Legas, cibiyar kasuwanci Najeriya.

Darakta janar na hukumar agajin gaggawa ta jihar Legas, Oluwafemi Oke-Osanyintolu, ya fadawa manema labarai cewa, al'ummomin unguwannin Abule-Ado da Soba su ne wadanda matsalar ta fi yiwa mummunar barna a sakamakon fashewar da ta faru ranar Lahadi.

Akwai makarantu biyar, da coci uku, da otel guda, da kuma wani babban kanti wadanda fashewar ta lalata.

Haka zalika, kimanin gine gine 170 ne suka lalace a yankin a sanadiyyar gobara da ta barke wanda fashewar ta haddasa. Sannan akwai motocin hawa 40 da wasu manyan motoci uku duka sun lalace.

Oke-Osanyintolu ya ce gwamnan jihar Legas Babajide Sanwoolu, ya ba da umarnin tsugunar da mutanen da suka rasa muhallansu a yankin Igando, dake wajen birnin Legas.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China