2020-03-13 12:00:33 cri |
Mele Kyari, shugaban kamfanin mai na Nijeriya NNPC, ya bayyana a ranar Laraba cewa, kasar mafi karfin tattalin arziki a Afrika, ta fara ganin tasirin faduwar farashin, yana mai cewa, idan kasuwar mai ta rushe, to komai zai rushe, musammam a kasa kamar Nijeriya da ta dogara da man fetur.
Ita ma Angola, kasa ta biyu mafi fitar da man fetur bayan Nijeriya, na fuskantar kalubale, inda bangaren man ya gamu da tasgaro.
Hukumar samar da man fetur da iskar gas da makamashi mai tsafta ta Angola, ta ce har yanzu tana nazari kan tasirin faduwar farashin man a duniya. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China