Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
WHO ta nuna goyon baya ga Sin da ta tabbatar da mutanen da aka tantance su a asibiti da suka kamu da cutar COVID-19
2020-02-14 13:30:41        cri
Hukumar lafiya ta duniya wato WHO ta bayyana a jiya cewa, ta nuna goyon baya ga Sin da ta dauki matakin tabbatar da mutanen da aka tantance su a asibiti da suka kamu da cutar numfashi ta COVID-19 a lardin Hubei, a ganinta wannan ya taimakawa wadanda suka kamu da cutar wajen saukin samun jinya cikin sauri. Don haka, karuwar adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar ba ta shaida samun babban canji kan yanayin yaduwar cutar ba.

Hukumar kiwon lafiya ta lardin Hubei na kasar Sin ta sanar a jiya cewa, a ranar 12 ga wata yawan sabbin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar ya kai 14840, ciki har da mutane 13332 da aka tantancesu a asibiti bisa alamun kamuwa da cutar da suka nuna. Inda alkaluman sun jawo hankalin jama'a sosai.

Michael Ryan, shugaban kula da ayyukan kiwon lafiya cikin gaggawa na hukumar WHO ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana cewa, an samu karuwar yawan sabbin mutanen da aka tabbatar cewa sun kamu da cutar ne saboda an canja hanyar tabbatar da mutanen da suka kamu da cutar. A ganinsa, wannan ya sa likitoci suna iya tantance mutanen da suka kamu da cutar cikin sauri, domin babu bukatar a jira sakamakon binciken kimiyya da aka yi musu, ta hakan za a tabbatar da mutanen da suka kamu da cutar don a yi musu jinya cikin sauri. Haka zalika za a taimakawa mutanen da suka taba yin mu'amala da mutanen da suka kamu da cutar da sauran matakan kiwon lafiya cikin gaggawa. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China