Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Velayati: Sabon shirin zaman lafiyan yankin gabas ta tsakiya da Amurka ta gabatar yana cike da matsaloli
2020-01-31 15:48:48        cri
Mai baiwa jagoran Iran shawara kan harkokin kasashen waje Ali Akbar Velayati, ya bayyana cewa, sabon shirin wanzar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya da kasar Amurka ta sanar, yana fuskantar tarin matsaloli, kuma mafarkin da Amurka da Isra'ila ke fatan gani ba zai taba yin nasara ba.

A ranar 28 ga watan Janairu ne, shugaba Donald Trump na Amurka, ya sanar da wani shirin samar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, don goyon bayan mamayen matsugunan Palasdinawa da Isra'ila ke yi. Abubuwan da ke kushe cikin shirin dai, sun goyi bayan Isra'ila, da watsi da bukatun Palasdinawa, matakin da ya kara fuskantar rashin amincewa tsakanin galibin mazauna yankin gabas ta tsakiya, ciki har da Palasdinawa.

A jiya ne kuma, Palasdinawa da dama suka shirya gangami a wajen birnin Ramallah dake yammacin kogin Jordan don nuna rashin amincewarsu da shirin da Amurkar ta gabatar.

A wannan rana kuma, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, ya tattauna da firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a Moscow, domin jin ra'ayinsa game da shirin da shugaba Trump din ya gabatar. A halin yanzu dai, bangaren Rasha, bai fitar da wata sanarwa game da ganawar bangarorin biyu ba.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China