Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Boko Haram sun yi zagon kasa ga wutar lantarki a arewa maso gabashin Najeriya
2020-01-22 09:40:46        cri
Harin baya bayan nan da mayakan Boko Haram suka kaddamar a birnin Maiduguri dake shiyyar arewa maso gabashin Najeriya ya katse layukan wutar lantarki, lamarin da ya haifar da rashin wutar lantarki ga mazauna yankuna.

Lamarin wanda ya faru a Juma'ar da ta gabata ya haifarwa Maiduguri, babban birnin jahar Borno, katsewar hasken wutar lantarki, kamar yadda wata sanarwa daga kamfanin rarraba wutar lantarki ta Najeriya (TCN) ya fitar.

TCN, wanda shi ne ke da alhakin rarraba wutar lantarki a kasar, ya ce wasu mayakan Boko Haram sun lalata kayayyakin samar da lantarki a Maiduguri a lokacin da suka kaddamar da harin. Harin ya kuma yi sanadiyyar lalata wutar lantarkin a garin Damaturu, birnin dake makwabtaka da jahar Borno a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya.

A watan Yunin shekarar 2019, kamfanin samar da lantarki dake yankin ya zargi kungiyar Boko Haram da lalata na'urorin wutar lantarki a garin Molai, dake Maiduguri, lokacin da suka kaddamar da hari a yankin. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China