Xi Jinping ya bukaci a zurfafa yaki da cin hanci a bangaren hada-hadar kudi
A wajen cikakken zaman taro na kwamitin ladabtarwa na tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da aka yi yau Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kasarsa ta zurfafa ayyukan yaki da cin hanci da karbar toshiya a bangaren hada-hadar kudi, musamman ma rubanya kokarin yaki da cin hanci a kamfanonin gwamnati, da kara karfin daidaita albarkatu da dukiyoyin kasa, da kokarin gano matsalar cin hanci da karbar rashawa, dake tattare da hadarin karbar bashi a sassa daban-daban na kasar.(Murtala Zhang)
Labarai masu Nasaba