![]() |
|
2020-01-09 11:17:25 cri |
Xi, wanda kuma shi ne shugaban hukumar gudanarwar rundunar sojojin kasar ta Sin, ya yi wannan kira ne yayin wani taron gangami da aka yiwa lakabi da "Tsaiwa kan gaskiyar tushen akida." Ya kuma bayyana cewa idan har ana burin samun amincewar al'umma, to ya zama dole jam'iyya ta rungumi akidunta na ainihi.
An dai fara wannan gangami ne na 'yan jam'iyyar daga matakin sama zuwa kasa a zango biyu, tun daga watan Mayun shekarar da ta gabata, wanda tuni aka kammala kaso mai yawa na ayyukansa, wanda ya kunshi yayata hadin kai, da managarcin tsarin siyasa, da raya ayyuka a cikin jam'iyya. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China