Kasar Sin na fatan Iran da Amurka su kai zuciya nesa domin magance tsananta rikici tsakaninsu
2020-01-07 20:04:35 cri
Majalisar dokokin kasar Iran ta shigar da rundunar sojan kasar Amurka cikin jerin kungiyoyin ta'addanci, dangane da wannan batu, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a yau Talata cewa, ya kamata bangarorin da abin ya shafa su kai zuciya nesa, domin magance tsananta rikice-rikice a tsakaninsu. (Maryam)