Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin na mai da hankali matuka kan yanayin Gabas ta Tsakiya
2020-01-06 19:51:48        cri
Yau Litinin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana cewa, kasar Sin tana mai da hankali matuka kan yanayin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya, don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a wannan yanki yana da muhimmanci matuka ga duniya.

Dangane da karuwar sabanin dake tsakanin kasar Amurka da kasar Iran, Geng Shuang ya bayyana a yayin taron manema labarai a yau cewa, tsarin nuna karfin siyasa tsohon yayi ne kuma ba zai yi nasara ba. Matakin soja na rashin hankali na baya-bayan nan da kasar Amurka ta dauka, ya keta babbar ka'idar dangantakar kasa da kasa, lamarin da ya haifar da zaman tankiya a yankin. A ko da yaushe, kasar Sin tana adawa da amfani da matakan soja cikin harkokin kasa da kasa, domin ba za a iya warware matsala ta hanyar matakan soja na matsin lamba ba.

Yau Litinin, gwamnatin kasar Iran ta sanar da shiga mataki na 5 wajen dakatar da wasu tanade-tanade dake cikin yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran. Dangane da wannan lamari, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Geng Shuang ya yi kira ga dukkan bangarorin dake cikin yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran da su kai zuciya nesa, da kuma tsayawa tsayin daka wajen warware matsalar ta hanyar siyasa, da kiyaye yarjejeniyar bisa dukkan fannoni yadda ya kamata. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China