2019-12-12 10:25:18 cri |
Mr. Daramola wanda ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na Xinhua hakan, ya ce farmakin na ranar Talata, na da nufin kakkabe gyauran mayakan na Boko Haram daga wannan yanki, tare da datse musu damar kaddamar da hare-hare.
Yankin arewa maso gabashin Najeriya dai ya sha fama da tashe-tashen hankula masu nasaba da ayyukan kungiyar ta Boko Haram cikin kusan shekaru 10, inda a shekarar 2014 kungiyar ta yi garkuwa da 'yan mata da dama dake karatu a wata makarantar sakandare.
Burin kungiyar Boko Haram dai shi ne kafa abun da ta kira daular Islama, a kasar dake kan gaba wajen yawan al'umma a daukacin nahiyar Afirka. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China