Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kwamitin bincike na majalisar dokokin Amurka ya kada kuri'ar amincewa da rahoton neman tsige shugaba Trump
2019-12-04 11:29:07        cri
Kwamitin tattara bayanai dake karkashin jagorancin jam'iyyar Dimokarat na majalisar dokokin Amurka ya kada kuri'ar amincewa da rahoton binciken neman tsige shugaban kasar Amurka Donald Trump.

Kuri'u 13 na mambobin sun amince, yayin da mambobi 9 ba su goyi baya ba, da kwamitin tattara bayanai wanda ke karkashin jagorancin Adam Schiff ya mika rahoton binciken ga kwamitin harkokin shara'a na majalisar dokokin wanda zai jagoranci duba binciken neman tsige shugaban kasar kuma shi ne ke da alhakin tsara dukkan jadawalin matakan tsige shugaba Trump daga mukaminsa.

Kada kuri'ar na zuwa ne 'yan sa'o'i bayan da 'yan majalisar wakilai na jam'iyyar demokarat suka fitar da wani rahoto dake neman hujjoji game da zargin da ake yiwa mista Trump na aikata ba daidai ba da neman kawo cikas ga taron majalisar. Ta hanyar amfani da dan majalisa na jam'iyyar Republican Mark Meadows, wanda na hannun daman shugaba Trump ne, ya mayar da martani cikin gaggawa a sakon da ya wallafa ta shafinsa na twita game da kada kuri'ar, inda ya bayyana yunkurin tsige shugaban da cewa babu hujja, kuma siyasa ce karara. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China