2019-12-02 20:13:44 cri |
Wannan abun da Amurka ta yi ya shaida mummunar niyyarta ta lalata yankin Hong Kong, gami da kawo tsaiko ga ci gaban kasar Sin baki daya.
Sharhin ya kuma bada misalin cewa, kungiyar The National Endowment for Democracy ta Amurka ko kuma NED a takaice, wadda ke tallafawa 'yan hatsaniyar Hong Kong, ta rika hura wutar rikici a wasu kasashe da yankuna sama da dari a duk duniya, al'amarin da ya shaida irin aika-aikar da Amurka ta yi, wato ta nuna goyon-baya ga masu tada rigima kuma tana fakewa da kare hakkin dan Adam da demokuradiyya.(Murtala Zhang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China