Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Dokar Da Amurka Ta Zartas Ya Keta Hakkin Dan Adam Na Jama'ar Hong Kong
2019-12-02 11:02:41        cri
Bangarori daban daban a yankin Hong Kong suna ganin cewa, dokar da kasar Amurka ta zartas dangane da batun hakkin dan Adam da tsarin dimokuradiya na yankin Hong Kong na kasar Sin, ya nuna a fili kasar Amurka tana goyon baya masu tada kayar baya a Hong Kong, kana ta take hakkin dan Adam na jama'ar yankin.

Shugaban kungiyar 'yan kasuwar shige da fice na yankin Hong Kong na kasar Sin Lam Lung-on yana ganin cewa, kasar Amurka ta zartas da dokar ce domin soke matsayin Hong Kong na yanki mai ikon karbar harajin kwstam bisa dokar kansa, da kuma bata matsayin yankin Hong Kong na cibiyar cinikin kasa da kasa, da cibiyar hada-hadar kudi na kasa da kasa, da na cibiyar tashar jiragen ruwa ta kasa da kasa. Kana, dokar ta kuma bata moriyar kamfanonin kasar Amurka dake yankin Hong Kong, lamarin da ya bata ran kowa da kowa, watau babu wanda zai yi nasara

Shehu malami a jami'ar koyon Sinanci ta yankin Hong Kong, wato CUHK, Lau Siu-kai yana cewa, kasar Amurka tana take 'yancin gwamnatin kasar Sin wajen kula da yankin Hong Kong a fili. 'Yan siyasa a kasar Amurka suna goyon bayan masu tada kayar baya na yankin Hong Kong, domin yin amfani da su wajen hana bunkasuwar kasar Sin, lamarin da ya zama babban kalubale ga tsaron kasar Sin. Don haka, ya zama dole ga kasar Sin ta mai da martini kan kasar Amurka, kuma tabbas matakin ba zai yi wa Amurka dadi ba. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China