Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Hukumar UNOSSC da kungiyar matasa ta Shenzhen sun kaddamar da shirin horar da matasa masu sana'o'i daga kasashe masu tasowa
2019-09-22 15:38:54        cri
Ofishin kungiyar kasashe masu tasowa na MDD UNOSSC, da kungiyar matasa ta Shenzhen ta kasar Sin, sun kaddamar da shirin horar da matasa 10,000 masu sana'o'i, daga kasashe masu tasowa, musamman na nahiyar Afrika.

Daraktan UNOSSC, Jorge Chediek, da Chen Daixing, mamba a kwamitin gudanarwa na kungiyar matasa ta Shenzhen ta kasar Sin ne suka sanar da shirin na horar da matasa 10,000, yayin taron matasa kan yanayi, wanda ya gudana a hedkwatar MDD.

Jorge Chediek, ya ce shirin zai dauki matakai kan kare yanayi ta hanyar kirkire-kirkire bisa tallafawa matasa masu sana'o'i dake rajin magance sauyin yanayi.

A cewarsa, shirin zai samar da hidimomin taimako ga sana'o'in da suka kafu da wadanda ke tasowa a kasashe masu tasowa.

Ya kara da cewa, shirin na da nufin horar da matasa masu sana'o'i 10,000 a cikin shekaru 5 ta hanyar inganta ilimi da samar da horo da samar da kudi da kirkire-kirkire da fasahohin zamani, yana mai cewa, shirin zai kuma tallafa wajen rayawa da bada jari da shawarwari ga dabarun kasuwanci 100. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China