Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasashen Masar da Habasha da Sudan sun gaza cimma sakamako kan madatsar ruwan Habasha
2019-09-17 09:22:44        cri
Ma'aikatar noman rani ta kasar Masar ta bayyana cewa, har yanzu ba a cimma daidaito ba a tattaunawar da ministocin kasashen Masar da Habasha da Sudan suka yi kan fara aikin babban madatsar ruwan Habasha da aka gina a kan kogin Nilu da ya ratsa kasashen uku.

Wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar, ta bayyana cewa, tattaunawar ta kwanaki biyu da ta gudana a birnin Alkahira, ta mayar da hankali ne kan matakan cikewa da tafiyar da aikin madatsar ruwan, ba ta kuma tabo yadda za a aiwatar da wadannan matakai ba.

Haka kuma taron bai tabo wani takamamman batutuwa ba, saboda yadda kasar Habasha ta ki tattauna shawarar da Masar ta gabatarwa tsakanin kasashen biyu.

A baya dai kasar Masar ta gabatarwa Habasha shawara kan tattaunawar da suka yi tun farko, da kuma yarjejeniya bisa manufa da shugabannin kasashen biyu suka sanyawa hannu a watan Maris na shekarar 2015, wadda ta bayyana cewa, bangarorin uku sun amince kan dokokin cikewa da gudanar da madatsar ruwan. (Ibrahim Yaya)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China