Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An kaddamar da aikin nazari da kera wani tauraron dan Adam a Masar
2019-09-09 12:13:16        cri
A jiya Lahadi, an yi taron kaddamar da aikin nazari da kera wani tauraron dan Adam mai taken "Eygpt No.2" a birnin Alkahira, fadar mulkin kasar Masar. Kasar Sin da kasar Masar na son gudanar da wannan aiki tare, don samar da wannan tauraron dan Adam da zai taimakawa kasar Masar a fannonin tsara shirin bunkasa birane, da sarrafa albarkatun teku, da hasashen yanayi, da aikin noma, da dai sauransu.

Manyan jami'an da suka halarci taron sun hada da Mohanmed El-Koosy, shugaban zartaswa na hukumar zirga-zirgar kumbuna ta kasar Masar, da Liao Liqiang, jakadan kasar Sin a kasar Masar.

Mista Mohanmed El-Koosy ya bayyana a wajen taron cewa, kasar Masar ita ce kasa ta farko da ta yi hadin gwiwa da kasar Sin a fannin fasahar tauraron dan Adam, karkashin shawarar "Ziri Daya da Hanya Daya". Wannan aiki na nazari da kera tauraron dan Adam, a cewar El-Koosy, zai taka muhimmiyar rawa ga yunkurin kyautata yanayin hadin gwiwar kasashen 2 a wannan fanni.

A nasa bangare, jakadan kasar Sin a Masar Liao Liqiang ya ce, kasar Masar tana kan gaba a fannin zirga-zirgar kumbuna a nahiyar Afirka, kuma wannan aiki zai taimaka wajen daukaka matsayin kasar Masar a idanun al'ummun duniya, da karfafa zumuncin da ke tsakanin kasashen 2, da aza harsashi ga yunkurin raya wata al'umma mai makomar bai daya tsakanin bangarorin 2. (Bello Wang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China