Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kamfanin talabijin na kasar Sin Konka ya bude reshensa a Masar
2019-08-02 10:35:51        cri
Babban kamfanin talabijin na kasar Sin Konka ya sanar a jiya Alhamis cewa ya bude kamfanin LED TV a lardin Beni Suef, dake kudu da babban birnin kasar Masar.

Bayan zuba jarin dala miliyan 30, sabon kamfanin ya kuduri aniyar kera akwatin talabijin samfurin LED TV, kimanin 600,000, a kowace shekara, matakin da zai samar da guraben aikin yi sama da 600 ga mutanen Masar.

Kasar Masar tana da yawan jama'a, akwai kwanciyar hankali ta fuskar siyasa, kuma tana da ingantaccen muhallin zuba jari. Wadannan su ne dalilan da suka sanya kamfanin ya zabi kafa cibiyarsa a kasar, a cewar Zhou Chi, janar manajan kamfanin Konkan.

A zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, Zhou ya ce, kamfanin Konka dake Masar zai samar da kayayyakinsa ga kasuwannnin Afrika, kuma kasar Masar wata muhimmiyar kasa ce wajen bunkasa cigaban gamayyar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ta kasar Sin.

Shirin na hadin gwiwa ne, tsakanin kamfanin Konka da kamfanin samar da kayayyakin latironi na HOHO dake Masar. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China