![]() |
|
2019-09-05 19:44:25 cri |
Wu Haitao ya ce cikin shekaru 8 da suka gabata, Libya ta kasance cikin wani mawuyacin hali, inda al'ummar take shan fama da tashe-tashen hankula, yayin da yanayin tsaro da na jin kai a sassan dake kewayenta ke kara tabarbarewa.
Wu Haitao, ya bayyana hakan ne yayin da yake karin haske, game da halin da ake ciki a Libya, lokacin zaman kwamitin tsaron MDD da ya gudana a jiya Laraba.
Daga nan sai jami'in ya sake jan hankalin kasashen duniya, da su taka rawar gani, wajen zakulo hanyoyin kawo karshen tarbarwar dake wakana a Libyan. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China