Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Wakilin Sin a MDD ya bukaci kasashen duniya da su sauke nauyin dake wuyansu karkashin dokar jin kai ta kasa da kasa
2019-08-14 13:12:40        cri
Wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya yi kira ga gwamnatocin da abin ya shafa da bangarorin dake fada da juna, da su yi kokarin sauke nauyin dake bisa wuyansu bil-hakki da gaskiya, karkahsin dokar jin kai ta kasa da kasa.

Zhang Jun wanda ya bayyana hakan yayin taron kwamitin sulhun MDD game da yayata ta karfafa doka yayin tabbatar da ayyukan zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, ya ce, yarjeniyoyin da aka cimma a Geneva da ragowar yarjeniyoyi, sun kasance muhimman ka'idojin da suka shafi bil-Adam wadanda suka samu goyon bayan dukkan kasashen duniya.

Ya ce, a halin yanzu, yanayin tsaron duniya ya kasance mai hadari gami da sabbin abubuwan ban tsaro da ke sake kunno kai. An kara samun yaduwar tashin hankali na masu dauke da makamai a wasu shiyyoyin, lamarin da ya haifar da mummunar damuwa ga al'ummomin duniya.

Jami'in na kasar Sin ya ce, ya kamata a kowane yanayi, gwamnatoci su sauke nauyin dake bisa wuyansu ta hanyar martaba dokar jin kai ta kasa da kasa, kuma wannan tsari ba zai sauya ba. Yana mai cewa, idan har ba za a iya kaucewa tashin hankali ba, to, ya kamata a martaba ka'idojin dokar jin kai ta kasa da kasa, don hana amfani da karfi ba gaira ba dalili ko wasu ayyukan da za su yi mummunan tasiri ga harkokin jin kai.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China