Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
UNSC ta yi Allah wadai da harin ta'addanci na baya bayan nan a Najeriya
2019-08-01 10:58:28        cri
Kwamitin sulhun MDD (UNSC) ya yi Allah wadai da babbar murya na harin ta'addanci na baya bayan nan a arewa maso gabashin Najeriya wanda ya yi sanadiyyar hallaka mutane 65.

Cikin wata sanarwar da ta fitar, mambobin kwamitin kasashe 15 sun bayyana juyayi da ta'aziyya ga iyalan mutanen da harin ya rutsa da su, da kuma mutane da gwamnatin kasar ta yammacin Afrika.

UNSC ta yabawa kokarin da kasashen shiyyar karkashin tawagar dakarun hadin gwiwar wanzar da zaman lafiya na shiyyar, wadanda ke yaki da ayyukan ta'addanci, kana MDDr ta bukaci su kara azama wajen tabbatar da tsaron shiyyar.

Mambobin kwamitin sulhun sun yi tir da dukkan wani nau'in ta'addanci inda suka bayyana cewa shi ne barazana mafi tsanani ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.

Haka zalika, kwamitin MDD ya bukaci a binciko wadanda ke da alhakin kaddamar da hare-haren, da kungiyoyin dake tallafa musu, da masu samar musu da kudade, don gurfanar da su a gaban shara'a, kana an bukaci dukkan jihohin su hada gwiwa da gwamnatin Najeriya da hukumomin da abin ya shafa don tabbatar da zaman lafiya da tsaro. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China